
CLICK HERE TO WATCH FULL VIDEO NOW
Nagode Allah Mijina Gwarzo ne Har Yamin Ciki
Na Samu Ciki, Cewar Tsohuwar Jaruma Ummi Rahab
Amaryar shahararren mawaƙi, jarumi kuma furodusa a masana’antar Kannywood Shu’aibu Ahmed Abbas (Lilin Baba) kuma tsohuwar jarumar Kannywood, Rahama Saleh Ahmed (Ummi Rahab), ta sanar da cewa ta samu juna biyu.
Ummi Rahab ta bayar da wannan sanarwar ne a Instagram, inda ta saka hoton ta sanye da wata jar atamfa, ta na zaune a kan kujera ta na murmushi. Jaridar Fim Magazine ta rahoto.
Ummi Rahab da kan ta sanar da samun rabon da tayi
A saƙon da Ummi Rahab ɗin ta fitar ta rubuta da manyan baƙaƙe cewa:
“Ina ɗauke da juna biyu.”
Jarumar wacce ta bar fitowa a cikin finafinai tun bayan aurenta ta kuma yi kira ga masoyan ta da su taya ta murnar samun wannan abin arziƙin da tayi, inda har ta yi alƙawarin za ta bayar da tukwicin katin waya ga mutum 50 na farko da su ka tura saƙon murnar a ƙasan hoton nata.
A kalamanta:
“Idan na samu ‘comments’ ta hanyar rubuta ‘Congratulations’ a ƙarƙashin wannan hoton, zan ba da kyautan kati … ga mutane 50”.
Sai dai ba ta faɗi yawan katin da zata rabar ba a matsayin tukwicin ba.
Haka kuma amaryar ta Lilin Baba ba ta bayyana adadin yawan lokacin da ta kwashe tana ɗauke da juna biyun ba.
An taya ta murna sosai
Mutane da dama masu bibiyar ta a Instagram sun taya ta murna tare da yi mata fatan alheri.
Idan ba a manta ba dai anyi bikin Ummi Rahab da Lilin Baba a ranar Asabar, 18 ga watan Yuni, 2022, a Tudun Murtala, Kano, a kan sadaki N200,000.
Waliyyin ango jarumi Ali Nuhu, shine ya amsarwa Lilin Baba auren Ummi Rahab.
Ku Biyomu ta Shafikan mu na sadarwa